Iri | aukuwa |
---|---|
Kwanan watan | 2 ga Yuni, 2012 |
Wuri | Jihar Yobe |
Adadin waɗanda suka rasu | 8 |
Fasa gidan yarin Damaturu dai wani hari ne da wasu ƴan bindiga su 40, da ake kyautata zaton ƴan ƙungiyar Boko Haram ne suka kai a gidan yarin Jimeta da ke garin Damaturu babban birnin jihar Yobe a arewa maso gabashin Najeriya. Ana tunanin harin wani yunƙuri ne na ceto ƴan kungiyar Boko Haram ɗin da ke ɗaure.[1][2] Kimanin fursunoni 40 ne suka tsere daga gidan yarin; fursunoni bakwai da mai kula da gidan yari ɗaya sun mutu.[3] Fursunonin da suka tsere yawancinsu ƴan tawayen ne.[4]
© MMXXIII Rich X Search. We shall prevail. All rights reserved. Rich X Search